نتائج البحث: 6236
|
ترتيب الآية | رقم السورة | رقم الآية | الاية |
2359 | 20 | 11 | فلما أتاها نودي يا موسى |
| | | Sa'an nan a lõkacin da ya je mata, aka kira shi, "Ya Mũsã!" |
|
2360 | 20 | 12 | إني أنا ربك فاخلع نعليك إنك بالواد المقدس طوى |
| | | "Lalle ne, Nĩ ne Ubangijnka, sai ka ɗẽbe takalmanka Lalle ne kanã a rãfin nan abin tsarkakẽwa, ¦uwa." |
|
2361 | 20 | 13 | وأنا اخترتك فاستمع لما يوحى |
| | | "Kuma Nĩ Nã zãɓe ka. Sai ka saurãra ga abin da ake yin wahayi." |
|
2362 | 20 | 14 | إنني أنا الله لا إله إلا أنا فاعبدني وأقم الصلاة لذكري |
| | | "Lalle, Nĩ Ni ne Allah. Bãbu abin bautawa fãce Ni. Sai ka bauta Mini, kuma ka tsayar da salla dõmin tuna Ni." |
|
2363 | 20 | 15 | إن الساعة آتية أكاد أخفيها لتجزى كل نفس بما تسعى |
| | | "Lalle ne Sa'a mai zuwa ce, lnã kusa da In ɓõye ta dõmin a sãka wa dukan rai da abin da yake aikatãwa." |
|
2364 | 20 | 16 | فلا يصدنك عنها من لا يؤمن بها واتبع هواه فتردى |
| | | "Sabõda haka, kada wanda bã ya yin ĩmãni da ita kumaya bi son zuciyarsa, ya taushe ka daga gare ta har ka halaka." |
|
2365 | 20 | 17 | وما تلك بيمينك يا موسى |
| | | "Kuma wãce ce waccan ga dãmanka yã Mũsa!" |
|
2366 | 20 | 18 | قال هي عصاي أتوكأ عليها وأهش بها على غنمي ولي فيها مآرب أخرى |
| | | Ya ce: "Ita sandãta ce, inã dõgara a kanta, kuma inã kakkaɓar ganye da ita a kan ƙananan bisãshẽna kuma inã da waɗansu bukãtõci na dabam a gare ta." |
|
2367 | 20 | 19 | قال ألقها يا موسى |
| | | Ya ce: "Ka yi jĩfa da ĩta, yã Mũsã!" |
|
2368 | 20 | 20 | فألقاها فإذا هي حية تسعى |
| | | Sai ya jẽfa ta. Sai gã ta dabbar macĩjiya, tanã tafiya da gaggãwa. |
|