بسم الله الرحمن الرحيم

نتائج البحث: 6236
ترتيب الآيةرقم السورةرقم الآيةالاية
22621912يا يحيى خذ الكتاب بقوة وآتيناه الحكم صبيا
Yã Yahaya! Ka kãma littãfi da ƙarfi. Kuma Muka bã shi hukunci yanã yãro.
22631913وحنانا من لدنا وزكاة وكان تقيا
Kuma (Muka sanya shi) abin girmamãwa daga gunMu, kuma mai albarka, kuma ya kasance mai ɗã'ã da taƙawa.
22641914وبرا بوالديه ولم يكن جبارا عصيا
Kuma mai biyayya ga mahaifansa biyu, kuma bai kasance mai girman kai mai sãɓo ba.
22651915وسلام عليه يوم ولد ويوم يموت ويوم يبعث حيا
Kuma aminci ya tabbata a gare shi a rãnar da aka haife shi da rãnar da yake mutuwa da rãnar da ake tãyar da shi yanã mai rai.
22661916واذكر في الكتاب مريم إذ انتبذت من أهلها مكانا شرقيا
Kuma ka ambaci Maryamu a cikin Littãfi, a lõkacin da ta tsallake daga mutãnenta a wani wuri, a gẽfen gabas.
22671917فاتخذت من دونهم حجابا فأرسلنا إليها روحنا فتمثل لها بشرا سويا
Sa'an nan ta riƙi wani shãmaki daga barinsu. Sai Muka aika rũhinMu zuwa gare ta. Sai ya bayyana a gare ta da siffar mutum madaidaci.
22681918قالت إني أعوذ بالرحمن منك إن كنت تقيا
Ta ce: "Lalle nĩ inã nẽman tsari ga Mai, rahama daga gare ka, idan ka kasance mai tsaron addini!"
22691919قال إنما أنا رسول ربك لأهب لك غلاما زكيا
Ya ce: "Abin sani kawai, ni Manzon Ubangijinki ne dõmin in bãyar da wani yãro tsarkakke gare ki."
22701920قالت أنى يكون لي غلام ولم يمسسني بشر ولم أك بغيا
Ta ce: "A inã yãro zai kasance a gare ni alhãli kuwa wani mutum bai shãfe ni ba, kuma ban kasance kãruwa ba?"
22711921قال كذلك قال ربك هو علي هين ولنجعله آية للناس ورحمة منا وكان أمرا مقضيا
Ya ce: "Kamar wancan Ubangijinki Ya ce. Shĩ, a gare Ni mai sauƙi ne. Kuma dõmin Mu sanya shi wata alãma ga mutãne, kuma wata rahama ce daga gare Mu.' Kuma abin yã kasance wani al'amari hukuntacce."


0 ... 216.1 217.1 218.1 219.1 220.1 221.1 222.1 223.1 224.1 225.1 227.1 228.1 229.1 230.1 231.1 232.1 233.1 234.1 235.1 ... 623

إنتاج هذه المادة أخد: 0.02 ثانية


المغرب.كووم © ٢٠٠٩ - ١٤٣٠ © الحـمـد لله الـذي سـخـر لـنا هـذا :: وقف لله تعالى وصدقة جارية

42265731292011344471261446352251243331